1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An karya yarjejeniyar tsagaita wuta ta Yaman

Abdourahamane HassaneDecember 15, 2015

'Yan tawayen Houthis sun kashe mutane guda bakwai a cikin wasu hare-haren da suka kai a yankin gabashi na ƙasar.

https://p.dw.com/p/1HNu2
Jemen Kämpfe in Taiz
Hoto: picture-alliance/AP Photo/A. Alseddik

Wakilai na gwamnatin Yaman da na yan tawaye na ci gaba da tattaunawa da zumar samar da sulhu a ƙasar Suizeland a ƙarƙashin jagorancin Majalisar Ɗinkin Duniya.Sai dai rahotannin da ke zuwa mana daga Yaman na cewar 'yan tawayen Houthis sun kashe farar hula guda bakwai a cikin wasu ruwan bama-bamai da suka yi a yau duk kuwa da yarjejeniyar tsagaita wutar da aka saka hannu a kanta.

Tun a cikin watan Maris da ya wuce ake gwabza kazamin fada tsakanin dakarun gwamnati masu samun goyon bayan Saudiyya;da kuma mayaƙan 'yan tawaye Houthis 'yan Shi'a masu samu tallafi ƙasar Iran.