1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai wani sabon hari a Bama

November 4, 2013

Hare-haren 'yan bindiga na ƙara halaka rayukan al'umma a jihar Borno, inda a ƙasa da kwana uku aka kai hari sau biyu kuma aka hallaka kimanin mutane 60.

https://p.dw.com/p/1ABUv
This picture taken on April 30, 2013 shows a Nigerian soldier, part of the 'Operation Flush' patrolling in the remote northeast town of Baga, Borno State. Nigeria's military said on May 16, 2013 that it was ready to launch air strikes against Boko Haram Islamists as several thousand troops moved to the remote northeast to retake territory seized by the insurgents. AFP PHOTO/PIUS UTOMI EKPEI (Photo credit should read PIUS UTOMI EKPEI/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images/AFP

Rahotanni daga Maiduguri babban birnin jihar Borno sun bayyana cewa, wasu mutane da ake kyautata za ton 'yan ƙungiyar Boko Haram ne, sun kai wani sabon farmaki a wani ƙauya kusa da Bama, inda suka hallaka mutane kimanin 30, yayinda suka jikka wasu dadama, kana suka kone gidaje sama 300. Wani jami'in ƙaramarhukumar Bama yace, maharan kimanin 70 dauke makamai, a kan babru 15, da motocin akori-kura, sun dira a ƙauyenne ba zato. Matsalar katse sadarwa a jihar Borno ta ƙara dagula al'amura, inda ƙauyawa basu da wata hanya ta sanarda halinda suke ciki koda wane kisan gilla da ake yi musu. Domin kuwa gwamnati ta katse sadarwa tun lokacin aka ƙaddamar da dokar ta-ɓaci. Jimi'in da ya bada labarin, yace harin da akai, ya zo ne bayan da a ƙarshen mako wasu 'yan bindi su ka yi wa wasu mutane dake dawowa daga daurin aure kwantan ɓauna, inda nan ma suka kashe 30 cikin harda ango. Maharan dai sun kashe dabbobi, kana suka lalata shaguna tare da yin sata ta kimanin Naira miliyan hudu.

Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Saleh Umar Saleh