1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai wa 'yan sanda hari a Afghanistan

Mouhamadou Awal Balarabe
March 20, 2020

Wasu 'yan bindiga sun kashe 'yan sanda da sojoji 24 a lardun Zabul na Afghanistan a daidai lokacin da ake neman aiwatar da yarjejeniyar da aka kulla tsakanin kasar Amirka da kungiyar Taliban.

https://p.dw.com/p/3Zn8O
Karte Infografik Anschlag in der Region Sabul, Afghanistan DE

Akalla jami'an tsaro 24 sun gamu da ajalinsu a kudancin Afghanistan, bayan da wasu da ake zaton 'yan Taliban sanya da kakin 'yan sanda suka bude musu wuta a lokacin da suke barci. Gwamnan lardin Zabul Rahmatullah Yarmal ya  tabbatar da wannan labari, inda ma yai kara da cewa, maharan sun kwace motoci uku da makamai daga hannun 'yan sanda.  Sai dai kungiyar Taliban ba ta ce uffan game da abin da ya afku ba

Wannan harin dai ya kasance daya daga cikin mafi muni a Afghanistan tun bayan da Amirka da 'yan Taliban suka rattaba hannu kan  yarjejeniyar Doha kan batun janyewar sojojin kasashen waje daga Afghanistan a cikin watanni 14 masu zuwa. Sai dai gwamnatin Afghanistan da kungiyar Taliban ba su cimma daidaito kan sakin masu fafutuka da makamai 5,000  ba, wanda ke zama muhimmin mataki da Kabul ba ta amince da shi a yarjejeniyar Doha ba.