An kai hari yammacin Nijar
April 18, 2021Talla
Rahotannin sun baiyana cewa mahara sun farwa mutane ne a makabarta yayin da daga bisani suka bude wuta ga wasu mazauna kauyen.
A baya-bayan nan dai mahara sun zafafa kai hare-hare yankin Tillaberi da ya hada iyakokin kasashen Nijar din da Mali da kuma Burkina Faso. Tun daga farkon wannan shekarar akalla mutane dari 3 ne suka rasa rayukansu a wasu hare-hare 3 da aka kai yankin, sai dai har kawo yanzu babu wata kungiya da ta fito ta dauki alhakin kai hare-haren.