Sabuwar gwamnati a Kasar Lebanon
February 1, 2019Talla
Masana a kasar sun yi hasashen cewar sabuwar majalisar zartaswar kasar wacce ta kunshi ministoci 30 daga jam'iyyin adawa za ta fusakanci kalubalen tattalin arziki kasancewar kasar wacce tafi kowacce kasa tulin bashi yanzu, tun bayan bullar rikici a kasar Siriya rashin aikin yi ya karu a Lebanon da kaso 20 tsakanin shekara ta 2011 zuwa shekara ta 2014 lamarin da ya zuwa yanzu gwamnatin ta gagara magancewa.
Kungiyar Hezbollah wacce kasar Amirka ta ayyana a matsayin kungiyar ta'adda na daga cikin wadanda mambobinta biyu suka rabauta da mukaman ministoci cikin sabuwar gwamnatin hadakar.