1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An gurfanar da waɗanda suka yunƙurin juuyin mulki a Burundi

Abdourahamane HassaneMay 17, 2015

Sojoji kusan 18 aka gurfanar a gaban kotu waɗanda ake zargi da kitsa juyin mulkin da ya ci tura.

https://p.dw.com/p/1FQvb
Militärputsch in Burundi Polizei
Hoto: Getty Images/AFP/J. Huxta

Hukumomi a ƙasar Burundi sun gurfanar da wasu mutane guda 18 yawancinsu sojoji, a gaban kotu sakamakon yunƙurin juyin mulkin da ya ci tura wanda suka yi wa shugaba Pierre Nkurumziza.

Kamfanin dilanci labarai na Faransa AFP ya ambato wasu na kusa da waɗanda aka cafken, suna shaida cewar, galibin waɗanda aka kama suna da raunika a jikinsu, har suka ce daya daga cikinsu ya kurumce a kune ɗaya, saboda mummunar dukkar da aka yi masa a gidan kurkun da ake tsare da shi.