An gurfanar da waɗanda suka yunƙurin juuyin mulki a Burundi
May 17, 2015Talla
Hukumomi a ƙasar Burundi sun gurfanar da wasu mutane guda 18 yawancinsu sojoji, a gaban kotu sakamakon yunƙurin juyin mulkin da ya ci tura wanda suka yi wa shugaba Pierre Nkurumziza.
Kamfanin dilanci labarai na Faransa AFP ya ambato wasu na kusa da waɗanda aka cafken, suna shaida cewar, galibin waɗanda aka kama suna da raunika a jikinsu, har suka ce daya daga cikinsu ya kurumce a kune ɗaya, saboda mummunar dukkar da aka yi masa a gidan kurkun da ake tsare da shi.