1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An gano wani shirin al-Shabaab na kai sabbin hare-hare

Mohammad Nasiru AwalFebruary 10, 2016

'Yan takife a Somaliya sun shirya kai hare-hare a matsayin sojin gona na rundunar zaman lafiyar AU a kasar.

https://p.dw.com/p/1HtUQ
Al-Shabaab Kämpfer in Mogadishu
Hoto: picture-alliance/AP Photo/AP Photo/F. Abdi Warsameh

Sojojin wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afirka AU a Somaliya sun ce sun samu bayanan cewa sojojin sa kai masu alaka da kungiyar al-Kaida sun shirya kai hare-hare a Somaliya a cikin unifom na sojojin AU. Jami'ai suka ce mayakan kungiyar al-Shabaab sun sace rigunan sojoji daga wasu sansanonin rundunar AMISOM kuma 'yan tarzoman sun shirya yin sojin gona don kai hare-hare. A ranar 15 ga watan Janeru sojojin Kenya da dama da ke aiki karkashin lemar rundunar AMISOM sun salwanta a wani hari da al-Shabaab ta kai kan sansaninsu da ke garin El Adde na kudancin Somaliya. 'Yan tarzoman sun ce sun kashe sojoji fiye da 100 a harin kan sansanin da ke kusa da iyakar Somaliya da Kenya, amma har yanzu gwamnatin birnin Nairobi ba ta fid da alkaluman yawan sojonjinta da aka halaka ba.