1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Asalin wadda ta kai harin kunar bakin wake a birnin Ankara

Mohammad Nasiru AwalMarch 14, 2016

Akalla mutane 37 suka rasu sannan fiye da 120 suka samu raunuka a harin kunar bakin waken birnin Ankara da ke zama irinsa na uku a birnin.

https://p.dw.com/p/1ICri
Türkei Anschlag in Ankara
Hoto: picture-alliance/dpa/Str

Hukumomi a kasar Turkiyya sun ce sun iya gano asalin wata mace da ke zama daya daga cikin wadanda suka kai mummunan harin kunar bakin wake a birnin Ankara a ranar Lahadi. Majiyoyin hukumomin tsaron kasar ta Turkiyya sun ce 'yar kunar bakin waken ta fito ne daga yankin gabashin kasar, kana kuma memba ce a haramtacciyar kungiyar Kurdawa ta PKK. Alkalumman da gwamnati ta bayar na cewa akalla mutane 37 suka rasu sannan fiye da 120 sun samu raunuka a harin kunar bakin waken da aka kai da mota a wata tashar motocin bas da ke kusa da dandalin Kizilly da ke birnin na Ankara. Wannan harin dai shi ne na uku da ya auku a tsakiyar birnin na Ankara a tsukin watanni biyar.