An cafke mutane da aka zarga da laifi a rubzawar gini a Bangladesh
April 27, 2013Talla
Kwanaki ukku bayan rubtawar gini mai hawa Takwas a Bangladesh, har yanzu ana ci gaba da zakulo mutanen da suka makale cikin buraguzen wannan gini.
Kawo yanzu fiye da mutane 300 suka rasa rayuka a hadarin,wannan ya gudana a daidai lokacin da ma'aikatan masaku daban-daban dake cikin ginin ke kan aiki.
A jiya Juma'a dubunan jama'a a Dakka babban birnin kasar, sun shirya zanga-zanga, domin cilastawa gwamnati ta cafke wanda suka mallaki gidan, da kuma shugabanin masana'antu da ke ciki.A yau jami'an tsaro sun bada labarin damko mutane biyu daga cikin su, a yayin da sauran suka shiga halin buya.
Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Usman Shehu Usman