An buɗe taron ƙasa da ƙasa a Katar a kan canjin yanayi
November 26, 2012
Kimanin ƙasashen duniya 200 ne ake sa ran zuwan su a birnin Doha na ƙasar Ƙatar inda za su share makonni biyu su na tautaunawa a dangane da batun canjin yanayi a duniya. Shekaru 15 bayan wata yarjejeniyar da ƙasashen duniya suka sa wa hannu a ƙasar Japan da aka fi sani da sunan yarjejeniyar Kyoto, kawo yanzu dai babu wani sauyin da aka gani daga manyan ƙasashen da suka rattaba hannu a kan yarjejeniyar. Duk da yake a shekara ta 1997 a ƙalla ƙasashe 40 ne suka amunce da rage budada hayakin gubar da suke sarrafawa daga kamfanoninsu a shekara, ta nan da wannan shekara ta 2012 , kawo yanzu babu wani takamaiman ci-gaban da aka samu daga ƙasashen.
Dama tun can farko ƙasar China ta bi sahun ƙasar Amurka gurin kin amuncewa da sa hannu a wannan yarjejeniyar. Yanzu haka masu lura da al'amura na ganin ko yanzu babu wani abun da za a cimma muddun ƙasasehn biyu har da Kanada ba su ɗauki nauyin da ya rataya a kansu ba a matsayinsu na manyan ƙasashen duniya.
Mawallafi: Issoufou Mamane
Edita: Mohammad Nasiru Awal