1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amnesty ta ce an kashe yara kankana a Mosul

December 22, 2016

A cikin wani rahoton da ta baiyana Kungiyar kare hakin bil Adama ta Amnesty International ta ce, yara kanana da dama sun galabaita wasu ma an jikkatasu a yakin da ake yi a Iraki

https://p.dw.com/p/2UhiP
Ein Jahr IS-Kalifat - Kids from Mosul
Hoto: DW/A. al Qaisi

Wata jami'ar kungiyar ta ce ta gana da wasu yaran wadanda suka sha azaba da arkane, yayin da wasu ma aka karkashesu a birnin na Mosul a yakin da ake yi tsakanin dakarun gwamnati da na 'yan tawaye. Muna wata matar da ta ba da shaidu a cikin rahoton ta ce, ta rasa ya'yanta 'yan mata guda biyu 'yan shekaru takwas da 14 a cikin barin wutar da ake yi ba dare ba rana a birnin na Mosul. Watanni biyu ke nan da suka wuce sojojin Iraki da ke samun goyon bayan kasashen duniya ke kokarin korar 'yan tawayen na IS daga Mosul.