1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Antony Blinken zai kai ziyara kasar Habasha

Ramatu Garba Baba
March 10, 2023

Sakataren Harkokin Wajen Amirka zai kai wata ziyara aiki a kasar Habasha da zummar shiga tsakani don warware rikicin da ke neman raba kasar biyu.

https://p.dw.com/p/4OXBq
Yan kasar Habasha da rikici ya raba da gidajensu
Yan kasar Habasha da rikici ya raba da gidajensuHoto: Mahmoud Hjaj/AA/picture alliance

A mako mai zuwa, Sakataren Harkokin Wajen Amirka Antony Blinken zai gana da firaministan kasar Habasha Abiy Ahmed da jagororin yankin Tigray a wata ziyarar aiki da zai kai yankin da ya sha fama da rikici. Ana sa ran ziyarar Blinken za ta taimaka wajen warware rikici a tsakanin bangarorin biyu da ke barazana ga kasar da ke yankin Kahon Afirka. An kwashi sama da shekara daya ana fada a tsakanin rundunar gwamnati da na 'yan tawayen TPLF, rikicin da ya yi sanadiyar salwantar daruruwan rayuka baya ga wasu kusan miliyan daya da suka rasa gidajensu.