1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Za a kai Saudiyya kotu bisa harbe-harben da sojinta ya yi

February 23, 2021

Iyalan mutanen da harbin da sojin saman Saudiyya Mohammed Saeed Alshamrani ya yi a barikin sojan ruwan Amirka a 2019 sun shirya kai karar kasar Saudiyya a kan lamarin. 

https://p.dw.com/p/3pjbq
USA Tödliches Pensacola-Marineschießerei
Hoto: picture-alliance/Zumapress/US Navy/P. Nichols

Takardun shigar da karar da aka rubuta a ranar Litinin sun yi zargin cewa Saudiyya na da masaniya cewa Alshamrani soja ne mai tsastsauran ra'ayi kuma ya na da alaka da kungiyar al-Qaida amma duk da haka Saudiyyar ta tura mata shi a cikin sojojinta da suka je barikin sojin ruwa na Florida domin yin wani kwas na soja.

Bude wutar da sojan na Saudiyya dai ya yi a ranar 06.12.2019 ta kai ga mutuwar sojojin Amirka uku da suka mutu bayan da ya bindige su.