Gwamnatin Trump ta sami nasara kan dokar hana shiga kasa
June 26, 2018Trump ya yaba da hukuncin kotun inda nan take ya yi shelar neman amincewar 'yan majalisar kasar don samun kudin da za a yi anfani a gina karin shingaye a kan iyakokin kasar.
Kotun ta yi watsi da bukatar da aka shigar gabanta kan cewa, dokar an tanade ta ne don nuna wariya ga al'ummar musulmi da ke sha'awar shiga kasar daga kasashen Iran da Siriya da Yemen da Somaliya da kuma Libya da wannan doka ta shafa. Mai shari'a Cif Justice John Roberts ya ce, kowanne shugaban kasa na da karfin iko kan dokokin shige da fice a kasa.
An kwashi tsawon watanni ana kai ruwa rana kan wannan batu bayan da Trump ya sanar da hana wasu kasashen duniya shiga kasar. Tun bayan shan rantsuwar soma aiki, shugaban ya sha alwashin kare muradun 'yan kasa dama tabbatar da tsaro ga daukacin al'umma.