SiyasaArewacin Amurka
Najeriya ta daina tauye damar addini inji Amirka
November 18, 2021Talla
Matakin da aka sanar a ranar Laraba na cikin jawabin da Blinken, inda ya ayyana sunayen kasashen da ke hana mutane yin addini yadda ya kamata. Kasashen da Amirka ta zayyana sun hada da Myanmar da China da Koriya ta Arewa da Saudiyya da Rasha da sauran wasu kasashe.
A shekarar da ta gabata Amirka ta sanya Najeriya cikin jerin kuma kawo yanzu ba ta bayar da dalilin janye sunan Najeriyar daga cikin jerin ba.
Ana dai sa ran sakataren harkokin wajen Amirkan zai isa Abuja a wannan Alhamis inda zai gana da Shugaba Muhammadu Buhari.