1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Aljeriya ta lashe kofin AFCON na 2019

Abdul-raheem Hassan MNA
July 20, 2019

Mahukuntan kasar Masar sun tsaurara matakan tsaro a filin wasan birnin Alkahira da kewaye, gabanin karawar tsakanin Senegal da Aljeriya.

https://p.dw.com/p/3MLhq
Ägypten Africa Cup of Nations 2019 | Finale Algerien gegen Senegal | Jubel
Hoto: Reuters/S. Salem

Kasar Aljeriya ta lashe gasar kwallon kafa na kofin nahiyar Afirka bayan lallasa kasar Senegal da ci daya da nema a wasan karshe da kasashen biyu suka fafata a daren ranar Jmum'a a kasar Masar.

Wannan dai shi ne karo na biyu da Algeriya ke daukar kofin bayan da ta yi nasarar daga kofin a shekarar 1990.

Tun dai bayan kammala wasan dubban mago bayan 'yan wasan Aljeriya ciki da wajen kasar ke shagulgilan nuna murna kan nasarar lashe kofin karo na biyu bayan shekaru 29.

Sai dai kasashe kamar Faransa an jibge 'yan sanda sama da 2000 a wani mataki na hana barkewar rikici tsakanin magoya bayan Aljeriya da Senegal.

Tun gabanin wasan mahukuntan kasar Masar sun tsaurara matakan tsaro a filin wasan birnin Alkahira da kewaye, gabanin karawar tsakanin Senegal da Aljeriya.