1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane biyar za su yi takara a Aljeriya

Abdul-raheem Hassan
November 3, 2019

Hukumar zaben kasar Aljeriya ta sanar da sunayen mutane biyar kacal da za su fafata a takarar neman shugabancin kasar tun bayan boren da ya kawo karshen wa'adin Abdelaziz Bouteflika.

https://p.dw.com/p/3SOHe
Algerien, Freitagsdemo
Hoto: picture-alliance/AP Photo/A. Belghoul

'Yan takara 23 ne suka mika takaradun nuna sha'awar tsayawa takarar shugaban kasar Aljeriya bayan jerin zanga-zanagar da ya kawo karshen mulkin Abdelaziz Bouteflika..

Yanzu haka dai sunayen mutane biyar ne hukumar zaben kasar ta amince tare da mika wa majalisar zartaswar domin tabbatar da takararsu. A watan Afirilun shrekarar 2019 ne sojoji suka tilasta wa Shugaba Abdelaziz Bouteflika. yin murabus bayan shafe shekaru 20 a kan mulki.