1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan na son sasantawa da kasashen yamma

Lateefa Mustapha Ja'afarJune 2, 2015

Shugaban kasar Sudan Omar Hassan al-Bashir ya ce zai bude shafin tattaunawa da kasashen yamma domin inganta dangantakarsu.

https://p.dw.com/p/1Faol
Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir
Shugaban kasar Sudan Omar al-BashirHoto: imago/Xinhua

Wannan mataki dai da Bashir ya sha alwashin dauka na zaman wani sabon abu a kasar da ta kwashe tsahon shekaru a karkashin takunkumin karya tattalin arziki daga al'ummomin kasa da kasa. Bashir ya bayyana hakan ne yayin da ya ke jawabi a gaban majalisar dokokin kasar jim kadan bayan sake rantsar da shi a matsayin sabon shugaban kasar ta Sudan, inda ya jaddada cewa ya dauki wannan kudirin ne da zuciya daya domin ganin dangantakar da ke tsakanin kasarsa da sauran kasashen yamma ta koma dai-dai. Tun dai a shekara ta 1989 ne Shugaba Omar Hassan al-Bashir ke kan karagar mulkin shugabancin Sudan bayan da ya jagorancin juyin mulki a kasar.