1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Al Bashir ya kafa kwamitin bincike

January 1, 2019

Shugaba Omar Hassan al Bashir na kasar Sudan, ya ba da umurnin gudanar da cikakken bincike kan zanga-zangar da ta mamaye kasar na sama da mako guda.

https://p.dw.com/p/3ArJx
Sudan Khartoum - Sudans Präsident - Omar Bashir
Hoto: picture-alliance/Xinhua News Agency/M. Khidir

Shugaba al Bashir ya bukaci ministan shari'ar kasar Mohammad Ahmad Salem da ya jagoranci kwamitin binciken, sai dai bai fayyace takaimaimen abin da za a bincika ba.

Matakin na zuwa ne bayan kiraye-kirayen da kasashen Amirka da Birtaniya da ma kungiyoyin kare hakkin bil'adama suka yi na a bincika amfani da makaman da jami'an tsaro suka yi da suka kai ga kisan wasu.

Zanga-zangar da aka fara da batun tsadar rayuwa, ta rikide ta koma neman murabus din Shugaba al Bashir, wanda ya yi shekaru 29 yana mulki a Sudan.