1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

al-Abadi: Ina so in sake jagorantar Iraki

Mouhamadou Awal Balarabe
July 13, 2019

Tsohon firaministan IraKi Haidar al-Abadi ya nuna sha'awar sake jagorantar kasar Iraki don magance matsalolin tsaro da cin hanci da rashawa da suka addabi kasar, lamarin da ya sa jama'a ke nuna bacin ransu.

https://p.dw.com/p/3M1wa
Parlamentswahlen im Irak Haider al-Abadi
Hoto: picture-alliance/dpa/AP

Tsohon firaministan Iraki Haidar al-Abadi ya ce a shirye yake ya sake zawarcin kujerar mulki sakamakon kalubalen da kasar ke fuskanta musamman a fannin cin hanci da rashawa da kuma rikicin addini. Wannan sanarwa ta zo ne a daidai lokacin da 'yan Iraki ke bayyana rashin jin dadinsu dangane da salon mulkin gwamnati da ke ci yanzu, inda katsewar wutar lantarki ke neman zama ruwan dare duk da tsananin zafi da ake fama da shi. 

Al-Abadi na rubanya tarurruka da shugabannin dabam-dabam ciki har da Ayatullah Ali Sistani, wanda goyon bayansa ke da mahimmanci wajen samun mukamin firaministan kasar Iraki. Shi dai Haidar al-Abadi ya kasance firaminista dan Shi'a daya tilo da aka yi wa tarba ta arziki a lardunan 'yan Sunni da yaki ya daidaita bayan da ya bayyana nasarar murkushe kungiyar IS a karshen shekara ta 2017. sai dai Firaministan da ke ci yanzu  Adel Abdel Mahdiya karyata jita-jitar da ake yayatawa game da aniyarsa ta yin murabus.