1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Afrika ta Kudu ta tura dakarunta Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

January 6, 2013

Afrika ta Kudu ta ce ta tura sojojinta dari hudu zuwa Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya domin tallafawa takwarorinsu a rikicin da ake yi tsakanin gwamnati da 'yan tawayen Seleka.

https://p.dw.com/p/17ExN
The commander of the regional African force FOMAC Jean-Felix Akaga reviews troops, on January 2, 2013 in Bangui after a press conference during which he warned rebels from the SELEKA coalition in the Central African Republic against any attempt to take Damara, the last strategic town between them and the country's capital Bangui, saying it would 'amount to a declaration of war.' The rebels, who began their campaign a month ago and have taken several key towns and cities, have accused Central African Republic leader Francois Bozize of failing to honor a 2007 peace deal. AFP PHOTO/ SIA KAMBOU (Photo credit should read SIA KAMBOU/AFP/Getty Images)
Zentralafrika Konflikt FOMACHoto: SIA KAMBOU/AFP/Getty Images

Fadar gwamnatin Afrika ta Kudun ce ta tabbatar da wannan labarin a wannan Lahadin inda ta ce gwamnatin shugaba Jacob Zuma ta dauki wannan matakin ne duba da yadda lamura na tsaro su ke cigaba da tabarbarewa a kasar.

Sanarwar har wa yau ta ce dakarun na Afrika ta Kudu za su bada gudumawa wajen ganin an raba 'yan tawaye da makaman da su ke dauke da su da kuma kokarin ganin an daidaita sahunsu inda za su shiga cikin sauran al'umma domin gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum kamar kowa.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki biyu gabannin tattaunawa da za a yi tsakanin 'yan tawayen na Seleka da gwamnatin ta shugaba Francois Bozize.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Umaru Aliyu