1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Afirka ta Kudu za a karbe filayen noma a ba bakar fata

Gazali Abdou Tasawa
August 1, 2018

Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya sanar da shirin yi wa kundin tsarin mulkin kasar gyaran huska domin samun izinin karbe filayen noma daga hannun Turawa domin raba wa al'ummar bakar fata.

https://p.dw.com/p/32Phc
Biologische Landwirtschaft in Südafrika
Hoto: DW

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya sanar da cewa jam'iyyarsa ta ANC za ta bukaci yi wa kundin tsarin mulkin kasar gyaran huska domin samun izinin karbe filayen noma daga hannun Turawa ba tare da biyan kudin diyya ba domin raba su ga al'ummar bakar fata masu rinjaye kana mafi talauci a kasar ta Afirka ta Kudu. 

Ramaphosa ya sanar da wannan aniya tasa ce a wani jawabi da ya gabatar a gidan talabijin na kasar inda ya ce matakin zai taimaka ga bunkasar tattalin arzikin kasar. 

A kasar ta Afirka ta Kudu dai, shekaru 24 bayan kawo karshen mulkin wariyar launin fata, fararan fata ne ke mallakar kaso 73 daga cikin dari na filayen noma masu albarka, filayen da gwamnatin ke son amfani da karfi a nan gaba domin karbe su da kuma rarraba su ga bakar fata a kasar. 

Har ya zuwa wannan lokaci dai gwamnatin Afirka ta Kudu na sayen filayen ne daga hannun fararan fata domin raba wa bakar fata a kasar.