1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matasa 21 sun mutu a gidan rawa

Abdul-raheem Hassan
June 27, 2022

'Yan sanda na cigaba da bincike kan musabbabin mutuwar matasa da dama a wani gidan cin abinci da rawa a unguwar Scenery Park a karshen mako.

https://p.dw.com/p/4DHuw
Afirka ta Kudu I 'Yan sandan
Hoto: STRINGER/REUTERS

Afirka ta Kudu na alhinin mutuwar matasa fiye da 20  wasu daga cikinsu 'yan kasa da shekaru 13 a wata mashaya, Shugaban ‘yan sandan kasar Bheki Cele ya shaidawa manema labarai a lokacin da ya ziyarci wurin da lamarin ya faru, inda ya ce har yanzu bai iya bayyana abin da ya faru a wurin ba, amma ya ce wasu daga cikin wadanda abin ya shafa ‘yan shekaru 13 ne kawai.

Za a dauki samfurori daga gawarwakin zuwa dakin gwaje-gwaje masu guba a Cape Town don ƙarin bincike, in ji ministan. Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya jajantawa iyalan wadanda lamarin ya shafa. "Yayin da shugaban kasar ke jiran karin bayani kan lamarin, tunaninsa yana tare da iyalan da suka rasa ‘ya'yansu da kuma iyalan da ke jiran tabbatar da yadda lamarin ya shafa,” in ji sanarwar da fadar shugaban kasar ta fitar.

Sanarwar ta kara da cewa, shugaban kasar na sa ran doka za ta dauki matakin bayan binciken da aka yi kan lamarin. A halin yanzu dai ana ci gaba da gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin, kamar yadda kakakin ‘yan sandan gabashin Cape, Birgediya Thembinkosi Kinana ya shaida wa manema labarai tun da farko.

Hukumomin gwmanatin sun ce 'yan mata takwas da maza 13 ne suka mutu, an samu gawarwakin mutane 17 a wurin, yayin da sauran suka mutu a asibiti. Hukumomi dai na zargin lamari na da alaka da maye.

Yawancin wadanda abin ya shafa ana kyautata zaton dalibai ne da suke murnar kammala jarabawarsu ta sakandare a daren Asabar, dumk da cewa haryanzu babu tabbacin sanadiyyar mutuwar, amma  hukumomi na zargin maye a karancin shekaru.

Jama'a da dama sun taru a wurin suna kokarin neman 'yan uwa. Ministan ‘yan sanda Cel ya yi tattaki zuwa wurin da abin ya faru a Scenery Park, inda ya shaida wa dimbin jama'a cewa: "Kira na kan iyaye ne su ga cewa an kula da ‘ya'yansu, kira ga al'umma su ce ba za mu iya barin yaranmu su yi hakan ba. mutu." An watsa ziyarar tasa kai tsaye ta talabijin, a cewar kamfanin dillancin labaran Reuters.