SiyasaAfirka
Dan wasan Najeriya ya kamu da corona gab da AFCON
December 30, 2021Talla
Dan wasan kwallon kafar Najeriya Victor Osimhen ya kebe kansa bayan da aka same shi da cutar corona a wannan Alhamis. kungiyar Napoli ta gasar Lig 'Seria A' ta kasar Italiya ta yi wannan shela, inda ta nunar da cewa dan wasan mai shekaru 23 ya katse hulda da sauran jama'a na wani lokaci don gudun yada cutar .
Hakan dai na nufin cewa akwai yiwuwar Victor Osimhen ya kasa shiga gasar AFCON a kan kari, alhali yana daya daga cikin 'yan wasan da za su iya cire wa Super eagles kitse a wuta.
Sabon kamun da coronar ta yi masa da ke zama na biyu a gare shi na zuwa gab da a yi masa gwajin lafiya na karshe kafin ya tafi Afirka.