1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Abiy Ahmed ya kare dakarunsa kan kisan gilla

Abdul-raheem Hassan
July 7, 2022

Firaministan kasar Habasha Abiy Ahmed ya kare gwamnatinsa da sojojin kasar daga zargin sakaci da ake yi masa, biyo bayan kazamin kisan gilla da aka yi a baya-bayan nan a wani yanki mai fama da rikici.

https://p.dw.com/p/4DpS1
Habasha | Firaiminista Abiy Ahmed Ali
Hoto: Office of the Prime Minister Ethiopia/UPI Photo/Newscom/picture alliance

An kashe daruruwan mutane akasarinsu 'yan kabilar Amhara a cikin 'yan makonnin da suka gabata, a wasu hare-hare guda biyu da aka kai a yammacin Oromia, yankin da ya fi yawan jama'a a kasar, da kuma wanda rikicin kabilanci ya barke a 'yan shekarun nan.

Da aka yi wa 'yan majalisar tambayoyi game da zubar da jinin da aka yi a baya-bayan nan, Abiy ya yaba wa jami'an tsaron Habasha, ya kuma ce gwamnati na aiki ba dare ba rana domin kare fararen hula.

Gwamnati ta dora alhakin kisan kiyashin da aka yi a ranakun 18 ga watan Yuni da 4 ga watan Yuli, a kan 'yan kabilar Oromo a Qellem Wollega da West Wollega, a cewar kungiyar 'yan tawayen. Ba a tabbatar da adadin wadanda suka mutu a hukumance ba.