A Najeriya mazauna Garkida na neman dauki
February 22, 2020Talla
Mazaunan a garin na Garkida sun tabbatar da kone-kone da 'yan bindigar da ake zargin na Boko Haram ne suka yi ciki har da majami'u da gidajen fitattun 'ya'yan yankin.
Rahotanni na cewa mazauna garin na Garkida na cikin hali na dar-dar, bayan harin da 'yan bindiga suka kansu a ranar Juma'a.
Wani mazaunin garin, Manu Usman Bakari, wanda a ya tsare da iyalinsa, ya yi wa DW bayani tare da tabbatar da mutuwar wasu jami'an tsaro.
Galibin jamaa dai sun kaurace wa garin, saboda fargabar abin da ka yia kasancewa. An kuma kokawa kan rashin kasuwanni da shagunan sayar da magunguna.