1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

A kalla mutane 688 sun halaka a girgizar kasar Nepal

Yusuf BalaApril 25, 2015

Wannan bala'i dai ya zama mafi muni cikin shekaru tamanin a tarihin kasar da ke zama matalauciya daga yankin kudancin na Asiya.

https://p.dw.com/p/1FEr6
Nepal Kathmandu Starkes Erdbeben Durbar Square
Al'umma cikin rudani bayan girgizar kasaHoto: picture-alliance/AP Photo//N. Shrestha

Wata mummunar girgizar kasa da ta afkawa kasar Nepal da ke a kudancin yankin Asiya a ranar Asabar dinnan, ta yi sanadin kisan akalla mutane 718 a bala'in da ya shafi kusan kasashen hudu makota da lalata gine-gine da hanyoyi, abin da kuma ya sanya zamowar kankara cikin gaggawa daga tsaunin Mount Everest .

Wannan bala'i dai ya zama mafi muni cikin shekaru tamanin a tarihin kasar da ke zama matalauciya daga yankin kudancin na Asiya.

A kalla mutane 688 daga kasar ta Nepal sun halaka kamar yadda 'yan sanda suka tababatar wasu 20 suma sun rasu a Indiya shida a yankin Tibet wasu guda biyu a Bangladesh, wasu 'yan kasar China biyu suma sun rasu akan iyakar Nepal da China.

'Yan mintuna ne dai kafin karfe shabiyun rana girgizar mai karfin maki 7.8 ta afku a yankin kwarin Kathamandu mai yawan jama'a.