1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙasar Italiya ta ceto bakin haure

May 31, 2014

Sojojin ruwan na Italiya sun ceto baƙin haure masu neman shiga Turai sama da dubu uku.

https://p.dw.com/p/1C9zX
Hoto: Mauro Seminara/AFP/Getty Images

Sojojin ruwan Italiya da ke bakin gaɓar ruwan ƙasar sun bayyana ceto baƙin haure fiye da 3,500 da suka haɗa da ɗaruruwan mata da yara, waɗanda suka fito daga arewacin Afirka. Hukumomin ƙasar suka tabbatar da haka, a lokacin da Firamnistan ƙasar Matteo Renzi ya yi kira kan neman taimako daga Ƙungiyar Tarayyar Turai.

An ceto baƙin haure 'yan arewacin Afirka da Siriya sakamakon aikin da aka gudanar tun daga daren Jumma'a, kuma mafi yawan baƙin haure sun fito ne daga Siriya. Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce rashin gwamnatoci na gari a ƙasashen arewacin Afirka tun bayan juyin-juya hali ya ƙara dagula lamura. Yanzu haka baƙin hauren da aka ceto suna a tashoshin jiragen ruwa na Sicily da Lampedusa da ke ƙasar ta Italiya.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Abdourahamane Hassane