1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zuma na zargin kasashe makwabta da rura wutar kyamar baki.

Gazali Abdou Tasawa/LMJApril 27, 2015

Shugaban kasar Afrika ta Kudu Jakob Zuma ya kare kasarsa daga sukan da kasashen duniya ke yi mata biyo bayan kisan baki 'yan kasashen Afirka da aka yi a kasar.

https://p.dw.com/p/1FFp9
Jacob Zuma na Afirka ta Kudu
Jacob Zuma na Afirka ta KuduHoto: AFP/Getty Images/R. Bosch

A cikin wani jawabi da ya gabatar albarkacin samun 'yancin kan kasar Shugaba Zuma ya zargi kasashen Afrika musamman makwabtan kasar tasa da taimakawa wajan yaduwar wanann matsala ta kyamar baki a Afirka ta Kudu, yana mai zargin bakin da kin zama a kasashensu na asali. Shugaba Zuma ya ce wannan batu ne da ya kamata a tattauna a kansa a taron kungiyar kasashen kudancin Afirka ta SADEC dama na kungiyar Tarayyar Afrika AU, a cewarsa 'yan kasashen Afirka da ke kasarsa da dama ne suka bayyana dalillansu na zuwa Afirka ta Kudu da rashin gamsuwa da yanda shugabannin ksashensu ke tafiyar da mulki.