Ziyara yan majalisar turai a Darfur
July 5, 2007Talla
Yan majalisun ƙungiyar gamayya turai, sun bayyana sanarwa, a game da halin da ake cikin a yankin Darfur na ƙasar Sudan.
A sakamakon ziyara aikin da wakilan EU su ka kai a wannan yanki, sun ganewa idanun su matsanacin halin da al´ummomi ke ciki.
Shugabar tawagar yan majalisun tarayya turai, Josef Borrel ya sanar manema labarai cewar, yarjeniyar zaman lahia da a ka ratabawa hannu, a shekara da ta gabata, ba ta tsinana komai ba, wajen maido da kwanciyar hankali, a Darfur, inda har yanzu ƙungiyoyin tawaye ke cin karen su babu babbaka.
Tawagar ta yi kira ga Majalisar Ɗinkin Dunia, ta gaggauta aika rundunar ƙasa da ƙasa wadda a ka cimma daidato kanta tare da amincewar hukumomin Khartum.