Ziyara Hu JinTao a Afrika
April 25, 2006Shugaban ƙasar China, Hu JinTao na ci gaba da ziyara a nahiyar Afrika.
Bayan Marroko inda ya ke a halin yanzu Hu JinTao, zai ziyaraci Nigeria da Kenya.
A birnin Rabat, inda ya gana da Sarki Mohamed na 6, sun rattaba hannu a kan yarjeniyoyi 7, tsakanin ƙasashen su.
Wannan yarjejeniyoyi, sun shafi saye da sayarwa, ta takin zamani, da kayan gina , da harakokin yawan buda ido,sannan da bincike, ta fannin kimiyya da Fassaha.
A halin yanzu, ƙasar China ,ta kwace harakokin kasuwa tsakanin Afrika ta turai, inda ako wace shekara a ke ƙara samun hauhawar hajojin China, a cikin wannan nahiya.
A yayin da ya ke hira da manema labarai ,Hu JinTao ya tabbatar da cewa, China a shire take, ta kara hulɗa, da Afrika, sannan a game da hare haren ta´adacin da su ka wakana jiya a Masar, ya kira ga kasashen dunia da su tashi tsaye tsayin daka, domin magance matsalolin ta´adanci a dunia.