1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ziyara A. Merkel a Asia

August 27, 2007
https://p.dw.com/p/BuCz

Shugabar gwamnatin Jamus Angeller Merkel, ta fara rangadi kwanaki 6 a nahiyar Asia.

Merkel ta kai wannan rangadi da riga 2, na farko a matsayin ta, na shugabar ƙasa mafi ƙarfin tattalin arziki a turai, sai kuma na 2, a matsayin ta, na shugabar rukunin ƙasashe 8 masu ƙarfin tattalin arziki a dunia.

Mahimman batutuwan da ke ajendar wannan ziyara, sun haɗa da harakokin cinikaya, sai kuma batun yaƙi da gubatar yanayi.

Kazalika, Angeller Merkell,zata tanttana da hukumomin Sin, a game da rikicin yankin Darfur na ƙasar Sudan, ta la´akari da goyan bayan da Pekin ke baiwa Sudan.

Jim kaɗan bayan fara wannan rangadi, Merkell ta bayyana batutuwan da ke tafe da ita:

Kowa ya san da cewar Asia, yanki ne, mai muhimmanci, ta fannin tattalin arziki.

A matsayi na, na shugabar ƙasashen G8 ,za ni anfani da wannnan dama, domin yin bitar hulɗoɗi tsakanin Asia da ƙasashen na G8.

Za ni ziyarci Sin da Japon, a ƙasar Sin, za mu tantana da hukumomi, albarkacin cikwan shekaru 35, da ƙulla mu´amila tsakanin Jamus, da ƙasar.

A tsawan wannan lokaci, mun cimma nasarori masu yawa, ta fannonin saye da sayarwa da kuma al´adu.