1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zargin illata Lula da Silva a siyasance

Ahmed SalisuSeptember 15, 2016

Tsohon shugaban Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya ce zargin da ake masa kan cin hanci da rashawa wata kullalliya ce da aka shiryo da nufin yi masa illa a siyasance.

https://p.dw.com/p/1K3Ie
Brasilien PK Lula da Silva
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Moreira

Mr. Da Silva na wadannan kalamai ne bayan da masu gabatar da kara suka ce shi ne ya jagoraci wasu jami'an gwamnati wajen badakalar cin hanci da rashawa da aka tafka a kamfanin man kasar wato Petrobras. Tsohon shugaban wanda ke dasawa da Dilma Rouseff da aka tsige daga mukaminta na shugabancin kasar ya ce an shirya wannan abu ne don ganin tauraruwarsa ta dusashe kafin zaben gama-gari da za a yi a kasar cikin shekarar 2018.