1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zargin fyade a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

Ahmed SalisuAugust 19, 2015

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta sake samun korafi na cin zarafin mata a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya wanda ake zargin jami'an kiyaye zaman lafiya na MINUSCA da yi.

https://p.dw.com/p/1GI3w
UN-Soldaten in Mali
Hoto: picture-alliance/dpa/T. Bindra

Mai magana da yawun majalisar Vannina Maestracci ta shaidawa manema labarai dazu cewar wannan batu ya faru ne a 'yan makonnin da suka gabata, kuma iyalan wanda aka ciwa zarafin ne da kansu suka yi korafin.

Maestracci ta ce 'yan mata biyu da wata kankanuwar yarinya ce aka yi wa fyade sai dai ba ta bayyana suna ko kasar da sojojin da suka yi fyaden suka fito ba amma dai ta ce su uku ne.

A makon jiya sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon ya sallami shugaban rundunar ta MINUSCA Janar Babacar Gaye bayan da korafi kan zargin yi wa 'yan mata fyade ya yawaita.