1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga zangar magoya bayan Georges Weayah a birnin Monrovia

December 12, 2005
https://p.dw.com/p/BvGl

Wakilin Majalisar Dinkin Dunia a kasar Liberia ya nuna rashin gamsuwa da zanga zangar da magoyan bayan Dan takara zaben shugaban kasa Georges Weayah su ka shirya a birninMonrovia.

Tsakanin jiya da yau, masu zanga zangar sun jaddada kin aminceqwa da sakamakon shugaabnkasar da a ka yi wanda ya baiwa Madame Sirleaf Ellen Johson rinjaye.

Jami´an tsaro sun tarwatsa su, tare da amfani da barkonon tsohuwa.

Masharahanta su fara fassara al´ amarin tamkar wani muturkilin saka Liberia a sabin yake yake..

Jami´an tsaro sun capke da dama daga masu zanga zangar.

Kazalika, rundunar kwantar da tarzoma ta Majalisar Dinkin dunia, ta kara karfafa matakan tsaro a manya manyan titinan babban birnin kasar.

Kakakin rundunar yan sanda ta kasa, ya sanar cewa, da dama kuma daga jami´an tsaro sun samu raunuka.

Zanga zangar na gudana a yayin da sabuwar kasar, Ellen Searleaf Johson, ke ciki gaba da ziyara aiki, ta kwanaki 9 a kasar Amurika.

Searleaf Johson, na tantanawa da assusun bada lamani na dunia, da bankin dunia, domin samar da kudaden talafawa