Zanga zangar magoya bayan Georges Weayah a birnin Monrovia
December 12, 2005Wakilin Majalisar Dinkin Dunia a kasar Liberia ya nuna rashin gamsuwa da zanga zangar da magoyan bayan Dan takara zaben shugaban kasa Georges Weayah su ka shirya a birninMonrovia.
Tsakanin jiya da yau, masu zanga zangar sun jaddada kin aminceqwa da sakamakon shugaabnkasar da a ka yi wanda ya baiwa Madame Sirleaf Ellen Johson rinjaye.
Jami´an tsaro sun tarwatsa su, tare da amfani da barkonon tsohuwa.
Masharahanta su fara fassara al´ amarin tamkar wani muturkilin saka Liberia a sabin yake yake..
Jami´an tsaro sun capke da dama daga masu zanga zangar.
Kazalika, rundunar kwantar da tarzoma ta Majalisar Dinkin dunia, ta kara karfafa matakan tsaro a manya manyan titinan babban birnin kasar.
Kakakin rundunar yan sanda ta kasa, ya sanar cewa, da dama kuma daga jami´an tsaro sun samu raunuka.
Zanga zangar na gudana a yayin da sabuwar kasar, Ellen Searleaf Johson, ke ciki gaba da ziyara aiki, ta kwanaki 9 a kasar Amurika.
Searleaf Johson, na tantanawa da assusun bada lamani na dunia, da bankin dunia, domin samar da kudaden talafawa