Zanga-zangar adawa da mulki Kabila
February 24, 2018Talla
Kungiyar nan ta Lay Coordination Comittee (CLC) ce ta kira wannan zanga-zanga ta ranar Lahadi inda al'ummar kasar za su bazama kan tituna neman Kabila ya bar mulki. Gabannin fara wannan zanga-zanga, mabiya darikar Katolika da dama kasar sun gudanar da addu'o'i na musamman a jiya Juma'a, inda wasu daga cikin limaman cocin Katolikar kasa suka bukaci mabiya addinin Kirista da su shiga a dama da su a zanga-zangar wadda suka ce ta lumana ce.