1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaman zullumi a Cote d'Ivoire

November 26, 2010

Yayin da aka shiga ranar ƙarshe ta yaƙin neman Zaɓen zagaye na biyu, hankula sun tashi a Abidjan.

https://p.dw.com/p/QJDW
Yaƙin neman zaɓe a AbidjanHoto: Picture alliance/dpa

Tun kwaniki da Zaɓen ke kusatowa, zaman zullumi ya ƙaru matuƙa a ƙasar ta Cote d'Ivoire
, gabanin zaɓen zagaye na biyu da za'a yi jibi Lahdi. Zaɓen shine ake fatan ya kawo ƙarshen rashin jituwa da aka yi fama da shi, tun shekaru takwas da suka gabata, bayan da aka gwabza yaƙin basasa, abinda ya kai ga raba ƙasar gida biyu, kafin a samu sasantawar da ta kowa ƙwarya-kwaryan kwanciyar hankali a ƙasar dake yammacin Afirka. An dai samu tashin-tashina nan da can, tun a zaɓen shugaba ƙasar zagayen farko wanda aka yi a watan jiya, inda shugaba mai ci Lauren Gbagbo da tsohon Firimiyan ƙasar kuma wanda ya taɓa kasancewa babban jami'i a bankin duniya wato Alhassan Ouattara. A zaɓen na farko dai 'yan takaran biyu sunyi kan kankan, don haka yanzu za su shiga zagaye na biyu a jibi lahdi, da yardan mai duka.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu