1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zagon kasa ga aikin hakar mai a Nigeria

March 6, 2006
https://p.dw.com/p/Bv5v

Yayin da kungiyar kasashe masu arzikin mai na duniya OPEC ke shirin gudanar da wani muhimmin taro a mako mai zuwa, a birbnin Vienna, a wage guda kuma tsagerun matasan yankin Niger Delta a Nigeria, sun lashi takobin dakatar da hako mai a yankin da kimanin ganga miliyan daya. A can baya, sakamakon hare hare a kan bututun mai ya sanya kasar ta rage yawan man da ta ke hakowa da ganga 445,000. Nigeria dai na hako danyen mai ganga miliyan biyu da rabi a kowace rana. Yan takifen na Niger Delta sun sha nanata kai farmaki a kan rijiyoyin man har sai gwamnati ta biya musu bukatun su.