Zagayowar shekaru biyu da aukuwar igiyar ruwan Tsunami
December 26, 2006Talla
Kasashen nahiyar Asiya masu iyaka da tekun Indiya suna gudanar da bukukuwan tunawa da bala´in igiyar ruwan nan ta Tsunami wadda ta auku shekaru biyu da suka wuce. Wata girgizar kasa mai karfin awo 9 a ma´aunin richter da ta auku a karkashin teku a can kusa da tsibirin Sumatra na kasar Indonesia a ranar 26 ga watan desamban shekara ta 2004, ta janyo igiyar ruwa wadda ta halaka mutane kimanin dubu 230. Lardin Aceh na Indonesia ya bala´in ya fi shafa, inda mutane dubu 167 suka rasu sannan har yanzu dubban mutane ke ci-gaba da zama a gidajen wucin gadi. A kuma halin da ake ciki ana gudanar da wani aikin ceto a yankin bayan wata ambaliyar ruwa da ta yi sanadiyar mutuwar akalla mutane 80 yayin da dubu 100 suka tsere zuwa kan tuddai.