Zaben yan majalisun dokoki a Kongo
June 24, 2007Talla
Al´ummomin kasar Kongo sun gudanar da zaben yan majalisun dokoki a yau lahadi.
Saidai jam´iyun adawa sun karacewa wannan zabe, a dalili da abun da su ka kira arigizon kuri´u, da shugaba Denis Sassou NGuesso ya shirya, da zumar samun gagaramin rinjaye.
Rahottani daga kasar sun nunar da cewa, a birnin Pointe Noire da Brazaville, mutane ba su hito ba da himma a rufunan zabe, sannan a wurare da dama , an fara zaben tare da jinkiri mai yawa.
Baki daya, yan takara fiye da dubu daya su ka shiga wannan zabe.
Kungiyoyin fara hulla, a kasar, sun hango cewar , zaben ba shi da wani armashi, ko da ya samu halartar jam´iyun adawa, ta la´akari da matakan da gwamnati ta dauka na tabka magudi, da nufi samun gagaramar nasara.