1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a tattauna batun Gambiya a Ghana

January 6, 2017

Shugabannin da za su je bikin rantsar da sabon shugaban kasar na Ghana dabra da taron za su tattauna rikicin siyasar Gambiya.

https://p.dw.com/p/2VQRq
Gambia Präsident Yahya Jammeh & Nigerias Präsident Muhammadu Buhari
Hoto: Reuters

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya mai shiga tsakanin a rikicin siyasa na Gambiya,inda shugaba Yahya jammeh ya fadi a zaben shugaban kasa ya yi mursisi ya ki sauka.Ya ce a gobe Asabar a wajen taron rantsar da sabon shugaban kasar Ghana Nana Akufo Addo a  birnin Accra shugabannin kasashen na Afirka za su tattauna batun na Gambiya tare da samar da hanyoyin samun mafita a rikicin.Kakakin shugaban Najeriyar Garba Shehu wanda ya sanar da wannan labari ya ce Muhammadu Buhari ya sha alwashin warware matsalar siyasar ta Gambiya.