1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a gudanar taro kan rikicin Myanmar

March 30, 2013

Kungiyar kasashen Musulmai za ta yi taro bisa rikicin da ke faruwa a kasar Myanmar ko Burma

https://p.dw.com/p/187Bd
Muslims share relief food from private donors as they take refuge at a stadium in Meikhtila, Mandalay division, about 550 kilometers (340 miles) north of Yangon, Myanmar, Sunday, March.24, 2013. Myanmar's army took control of a ruined central city on Saturday, regaining control after several days of clashes between Buddhists and Muslims that killed dozens of people and left scores of buildings in flames in the worst sectarian bloodshed to hit the Southeast Asian nation this year.(AP Photo/Khin Maung Win)
Hoto: picture alliance/AP Photo

Kungiyar Hadin kan Musulmai ta bayyana a wannan Asabar cewa, ministoci daga Kungiyar Kasashen Musulmai na Duniya, za su gana ranar 14 ga wata mai kamawa na Afrilu a kasar Saudiya, domin tattaunawa kan rikicin da ke farauwa a kasar Mynmar ko Burma.

Sanarwar ta ce, za ayi ganawar a birnin Jeddah. Kafofin yada labaran kasar ta Myanmar sun bayyana karuwar mutanen da suka hallaka cikin rikicin na kwanaki 10, zuwa mutane 43, yayin da wasu 1300 suka rasa matsugunansu.

Mahukuntan kasar ta Myanmar sun bayyana daukan matakan da suka dace, domin dakile ruruwar rikicin tsakanin mabiya adddinin Budda da Musulmai.

mawallafi: Suleiman Babayo

Edita: Halima Balaraba Abbas