1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a fara shari'ar 'yan Boko Haram a Najeriya

Abdul-raheem Hassan MNA
October 9, 2017

A wannan Litinin za a gurfanar da sama da mutane 1600 da ake zargi 'yan Boko Haram a gaban shari'a, sai dai masu fashin baki a kan al'amuran shari'a na kalubalantar matakin gudanar da shari'ar cikin sirri.

https://p.dw.com/p/2lU38
Boko Haram
Hoto: Java

An dai bayyana gabatar da mutanen ne ba tare da inda jama'a suka sani ba, kazalika an yi niyar haramta wa 'yan jaridu da kungiyoyi halartar zaman shari'ar da za a fara a wannan Litinin.

Wadanda ake zargi da ayyukan ta'addancin da za a gabatar da su gaban kuliya, suna a tsare sama da shekaru takwas tun bayan bullar kungiyar Boko Haram. A yanzu ana zargin mutanen da haddasa asarar rayuka akalla fararen hula da jami'an gwamnati sama da dubu 20 a yakunan Arewa maso Gabashin Najeriya.

Wata kididdigar hukuma ta nuna cewa gabannin shari'ar da za a fara a wannan Litinin, mutane tara ne kadai aka yankewa hukunci a cikin mutane 13 da suka fuskanci shari'a a kan zarginsu da ayyukan kungiyar ta Boko Haram.