1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaɓen shugaban ƙasa a Rwanda

August 9, 2010

Al'umar Rwanda sun fara kaɗa ƙuri'unsu da nufin zaɓen shugaban kasa

https://p.dw.com/p/OfFV

A yau ne ƙasar Rwanda ke gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da ke zama irinsa na biyu tun bayan yaƙin basasa da ƙasar ta fiskanta a shekarar 1994. Duk da cewa 'yan takara uku ne ke ƙalubalantar Paul Kagame mai shekaru 52 da haihuwa, amma kuma manazarta sun yi hasashen cewa shugaba mai barin gado zai samu damar sabonta wa'adin mulkinsa na shekaru bakwai.

Shi dai Paul Kagame da ya kafa jam'iyar FPR ya ɗare kan karagamar mulki shekaru 16 da suka gabata, bayan da masu tsattsauran ra'ayi na ƙabilar Hutu suka aiwatar da kisan ƙare dangi a kan mutane dubu 800 na ƙabilar shugaban wato Tutsi. Mutane miliyan biyar ne suka yi rajista a ƙasar ta Rwanda domin kaɗa kuri'unsu a zaɓen na yau.

Mawallafi: Mouhamadou Awal Balarabe

Edita: Mohammad Nasiru Awal