UMP ta sha kayi a zaɓen jihohin Faransa
March 22, 2010Jam´iyar PS a ƙasar Faransa ta samu nasara a zagaye na biyu na zaɓen jihohi da aka gudanar a jiha lahadi
A sakamakon da ofishin ministan cikin gida ya baiyana ya nuna cewa jam'iyyar ´yan gurguzu suna da kishi 54.15 cikin ɗari yayin da jam'iyar dake mulki ta shugaba Nikola Sarkozy ke da kishi 35,39 cikin ɗari na ƙuri´un da aka kaɗa
Wannan mummuna kayi da jam iyar ta Sarkozy ta sha tun can da ma babu wani mamaki da ake da shi dangane da yadda tun a zagaye na farko ´yan gurguzun suka yi nasara a jihohi da dama
Ko da shi ke jam´iyyar dake mulkin ta sha kashi a yanukunan da dama to amma duk da haka a jihohi kamar su Alsace da Guyane da Reunion jam'iyar ta UMP ta yi nasara
An gana tsakanin shugaban ƙasa Nicolas Sarkozy da Firaminista Francois Fillon wanda shine ya jagorancin yaƙin neman zaɓen inda suka tattauna butun garambawul na majalisar ministocin.
Yanzu haka akwai rahotanin da ba a tabbatar da gaskiyarsu ba dake nuna cewa wasu ministocin menbobin jam´iyar ta UMP sun fara murabus a sakamakon kaye da jam´iyyar ta sha wanda aka ƙiyesta cewa mimistocin 20 na jam´iyyar dake mulki suka tsaya takara a zaɓen kana suka sha kaye a yankunan daban daban
Waɗanda ke kusa da Firaministan sun ce shi kame ko kadɗn ba zai yi marabus ba daga masayin
da ya ke Magana akan zaɓen Firaministan Francoi Fillon ya ce:
Ba mu shawo kan jama´a ba su amince su yarda da mu,wannan na zaman kaye garemu ´yan jamiyyar UMP kuma ni da kaina na ɗauki alhakin rashin samun nasara a wannan zaɓe kuma zamu tattauna da shugaban ƙasa.
Yan gurguzun dai waɗanda suke da rinjaye a zaɓen tare da sauran jam´iyyun siyasar masu neman sauyi sune ke riƙe da kusan kishi biyu cikin ukku na jihihohin da ake da su a Faransa
Babbar magatakarda ta jam´iyar PS Martin Aubry ta ce zasu cikka alƙawarin da suka ɗauka ga jama´a:
Tun daga gobe zamu fara aiki a cikin jihohinmu, kuma za mu cikka alkawarin da muka ɗauka tun lokacin yaƙin neman zaɓe kan samar da aiki da kula da makomar matasa.
Wannan kaye dai da jam´iyar ta UMP ta sha ,na zaman abinda masu lura da al´ amuran siyasa ke kallon mataki na farko na faɗuwar jam`'iyar a zaben shugaban ƙasa da za a yi a shekara ta 2012
Ko da shike shugabanin jam´iyyar sun bada tabbacen cewa zasu ɓullo da sabon salon a zaɓuɓukan tafe masu fashin baki akan al amuran siyasa na hasashen cewa taɓargazan shugaba Sarkozy itace ta jayomasa wannan kaye
Namiam Frank wani mai yi sharhi ne aka al´amuran siya a ƙasar ta Faransa:
Kuskuren shugaba Sarkozy shine ummal iba´isar abin da suka girbe a yau.
Ana iya yin sauye sauye a kowace ƙasa amma wasu sauye saune dolene a yi watsi da su idan yan ƙasa ba su gamsu da su ba.
Mawwallafi: Abdourahman Hassane Edita: Yahouza Sadissou Madobi