1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yunkurin takaita bada mafaka a Jamus

Usman Shehu UsmanJanuary 29, 2016

Hadin kan jam'iyyu da ke mulki a kasar ne suka cimma wata yarjejeniyar yin kwaskwarima ga tsarin neman mafakar siyasa a kasar wanda yanzu ke kan gaba a fiye da ko wace a Turai wajen karban baki

https://p.dw.com/p/1HlbP
Deutschland Regierungskoalition Seehofer Merkel und Gabriel Symbolbild
Hoto: picture-alliance/AP Photo/B. von Jutrczenka

A bara kadai kasar Jamus ta shigar da sunayen mutane miliyan daya da suka nemi a basu mafakar siyasa. Kuma yanzu gwamnati na fatan takaita wannan lamarin. Jagoran jam'iyar SPD Sigmar Gabriel, yace kasashen Moroko, Tunisiya da Aljeriya a sasu a matsayin kasashen da ake zaman lafiya, wadanda ma'ana 'yan kasar basa bukatar mafakar siyasa. Kuma yace a yarjejeniyar da suka cimma za'a dakatar da bada visar hadewar iyalai na shekaru biyu. Kudurin dai na bukatar sa hannun majalisar dokoki da ta zartaswa kan ya zama doka.