1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yinwa ta ratsa a yankin kudancin Afrika

Yahouza SadissouSeptember 9, 2005

Mutane kimanin milliyon goma ke fama da matsananciyar yinwa, a kasashen yankin kudancin Afrika

https://p.dw.com/p/BvZn

Kungiyar bada taimakon raya kasa, ta Oxfam ta yi kira ga kasashen masu hanu da shuni, da kungiyoyin daban daban na bada agaji, da su gaggawta kai taimakon abinci a yankin kudanci Afrika, inda a kalla mutane million 10 ke fama da karancin abinci.

Kungiyar Oxfam ta gayyaci kasashen da su wa´aztu, da abinda ya wakana a Jamhuriya Niger, inda sai bayan watani 6 da kiran da gwamnati tayi, na tallafawa al´umma, kanan taimakon ya fara shiga, mussaman bayan da kafofin sadarwa su ka fara nuna hotunan mattatun dabbobi, da na yara kanana rammamu, da yinwa ta karmashe.Kuma a wannan lakoci taimakon ya yi kama da gociya bayan mari,

Oxfam ta ce ba ta kamata kasashen n masu karfin tattalinn arziki su yi kunnan uqwar shegu da billa´ijn da ke wakana ahalin yanzu a yankin kudanci Afrika.

A kalla tsabar kuddade billiar guda ne,a ke bukata, domin ceton rayukan talakawan wannan kasshe, da su ka tsinci kansu, a cikin mayuyacin hali.

A ko wace ran ata Allah, inji rahoton kungiyar Oxfam, kasashe masu ci gaban masana´antu, na ware dalla billiar guda, domin tallafawa manoman su, indan su ka amince su kebe kudin rana daya tak,na tallafin da su ke yi, ga harakokin nonam kasashen su, ya wadata,r a ceci rayukan millliyoyin jama´a nahiyar Afrika.

Idan ba a manta ba,a watan da ya gabata shugabanin kungiyar SADC da ta hada, kasashen yankin kudancin Afrika sun yi zaman taro a birnin Gaborone na Botswana inda su ka ja hankalin dunia, a game da bill´in yinwa da al´ummomin su ke fuskanta.

Saidai ya zuwa yanzu, babu ko kwandalla, da ta shiga da sunan taimako daga kasashen ketare.

Idan ba a yi ba takantsatsan an bi hanyar shiga matsayin yinwaer da ta gallabaita milliyoyin jama´a a Jamhuriya Niger.

Albarkacin wannan zaman taro, shuwagabanin sun yanke shawara game karfi, da hussa´o´i domin, daukar matakan rage raddadin matsalar, kamin a fara samun taimako daga kasashen dunia.

Sakatare Jannar na Majalisar Dinkin Dunia, Koffi Annan a wata fira da yayi da manema labarai ya tabatar da cewa, ba´ada bayan yankin Sahel, da na kudancin Afrika, Sudan,Habasha da Somalia, na daga cikin jerin kasashe da ya kamata a kaima tallafin abinci, na gaggawa, amma har yanzu Majalisar Dinkin Dunia, ta rufe ido ga matsalolin wannan kasashe.

Abinda ya fi daukar hankulla a halin da ake ciki, shine na taron Majalisar, da kuma kwaskwarimar da za ayi mata, sannan da batun yaki da ta´adanci.

A karshe, kungiyar Oxfam, a cikin wannan rahoto,ta gayaci shuwagabanin yankunan da ke fama da balla´in yinwar,, da su kara daukar matakan kulla da al´ummomin su, domin a halin yanzu,neman taimako daga ketare, ya zamma, tamkar jiran gawon shanu.