1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-hare na kara lalata Yemen

Lateefa Mustapha Ja'afarMay 23, 2016

Kimanin mutane 45 ne suka hallaka yayin wasu tagwayen hare-haren ta'addanci da aka kai a birnin Aden na kasar Yemen.

https://p.dw.com/p/1It4w
Harin IS a birnin Aden na Yemen
Harin IS a birnin Aden na YemenHoto: Reuters/F. Salman

Tuni dai kungiyar 'yan ta'addan IS da ke rajin kafa daular Musulunci ta dauki nauyin kai wannan hari. Harin na farko dai wani dan kunar bakin wake ne ya kai shi, inda ya tashi motarsa da ke makare da bama-bamai a kofar ofishin rundunar sojojin kasar dai dai lokacin da ake tantance sojojin da za a dauka aiki.

Hari na biyu kuwa an kai shi ne a kofar gidan wani babban jam'in tsaro, inda maharin ya tayar da bama-baman da ke daure a jikinsa cikin wasu taron sojoji da ke tsaye. A baya-bayan nan dai sojojin gwamnatin kasar da ke samun goyon bayan dakarun rundunar taron dangi wadda Saudiya ke wa jagoranci, na fuskantar hare-hare daga kungiyar 'yan ta'adda ta IS.