Yau ake maida hankali akan Darfur
September 17, 2006Talla
A yau ne ake sa ran masu fafutukar kare hakkin bil adama da shugabanin addinai a koina cikin duniya zasuyi zanga zanga da kuma taruka da nufin jawo hankulan jamaa game da halin da ake ciki a yankin Darfur na kasar Sudan.
A halin da ake ciki dai yanzu,shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya sake nanatawa sakataren Majalisar Dinkin Duniya Kofi Annan kin amincewarsa ga girke dakarun majalisar a yankin na Darfur da yaki yayi kaca kaca da shi.
A jiya asabar ne Firaministan Burtaniya Tony Blair yayiwa Sudan din tayin ihsani muddin dai ta kawo karshen rikicin na Darfur,amma in taki amincewa akwai yiwuwar lakaba mata takunkumi.