1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yara masu cutar Aids na samun Kulawa

Ibrahima Yakubu | Abdul-raheem Hassan
November 8, 2017

A karan farko a Najeriya an sami wata mace mai fama da ciwon HIV/AIDS ko Sida a Kaduna, da ke renon kananan yara marayu masu cutar kanjamau tare da ba su horo kan sana’o’in hannu da ba su ilimi.

https://p.dw.com/p/2nHSQ
AIDS-Test Westafrika
Hoto: AFP/Getty Images

Malama Aisha Usman ta kasance daya daga cikin shugabannin kungiyoyin mata masu fama da cutar HIV/Aids ko Sida a jihar Kaduna da ke Arewacin Najeriya, ta koma tattaro kananan yara marayu da ke fama da cutar wadan da iyayen su suka rasu sanadiyyar kamuwa da cutar da nufin karesu daga fuskantar tsangwama da kyama a cikin alumma.

A yanzu dai Aisha na ci gaba da ba wa irin wadannan yara kyakkyawar kula tare da ba su horo na musamman kan sanao'in hannu, tana kuma sa su a makarantun Boko da na Allo domin samun ilimin addini da na zamani ta yadda za su yi dogaro da kansu anan gaba.